Saturday, September 14, 2024
Home Muhimman Labarai Kotu ta tabbatar da zaben Ahmadu Fintiri a matsayin gwamnan Adamawa

Kotu ta tabbatar da zaben Ahmadu Fintiri a matsayin gwamnan Adamawa

Kotun daukaka kara da ke zamanta a Abuja ta tabbatar da Ahmadu Fintiri na jam’iyyar PDP a matsayin gwamnan jihar Adamawa bayan ta yi watsi da karar da Aishatu Binani ta jam’iyyar APC ta shigar kan rashin cancanta.

A hukuncin da Mai shari’a Tunde Awotoye ya shirya kuma mai shari’a Ebiowei Tobi ya karanta a yau Litinin, Kotun daukaka kara ta kuma bayar da umarnin biyan Naira dubu dari biyar a matsayin diya wa Fintiri.

Kotun daukaka kara ta fusata kan sanar da sakamakon zaben da shugaban hukumar Hudu Ari ya yi da wuri, inda ta kara da cewa batutuwa marasa hujja sun dabaibaye karar ta Binani.

Kotun ta jaddada cewa matakin da kwamishinan zabe na jihar ya dauka na bayyana Binani a matsayin wanda ta lashe zaben ya sabawa doka.

Wannan hukunci na kotun na yau tabbatar da hukuncin da kotun sharia zaben gwamna ta yanke a ranar 28 ga watan Oktoba inda ta yi watsi da karar da Binani ta shigar.

RELATED ARTICLES

Za A Fara Dandaƙe Masu Yi Wa Yara Fyaɗe

Ministan shari'a na Madagascar ya kare wani sabon kudiri a ranar Juma'a don hukunta masu yiwa kananan yara fyade. Kungiyar kare hakkin biladama ta ...

Kotu koli ta tabbatar da zaben shugaban kasa Tinubu

A yau Alhamis ne kotun koli ta tabbatar da nasarar da shugaba Bola Tinubu ya samu a zaben shugaban kasa da aka gudanar a...

Kotun koli za ta yanke hukunci kan zaben Tinubu gobe Alhamis

    A gobe  Alhamis, 26 ga Oktoba, 2023 ne dai kotun kolin za ta yanke hukunci kan shari’ar jam’iyyar Labour da dan takararta na shugaban...
- Advertisment -

Most Popular

Za A Fara Dandaƙe Masu Yi Wa Yara Fyaɗe

Ministan shari'a na Madagascar ya kare wani sabon kudiri a ranar Juma'a don hukunta masu yiwa kananan yara fyade. Kungiyar kare hakkin biladama ta ...

Kotu ta tabbatar da zaben Ahmadu Fintiri a matsayin gwamnan Adamawa

Kotun daukaka kara da ke zamanta a Abuja ta tabbatar da Ahmadu Fintiri na jam’iyyar PDP a matsayin gwamnan jihar Adamawa bayan ta yi...

Kotu koli ta tabbatar da zaben shugaban kasa Tinubu

A yau Alhamis ne kotun koli ta tabbatar da nasarar da shugaba Bola Tinubu ya samu a zaben shugaban kasa da aka gudanar a...

Kotun koli za ta yanke hukunci kan zaben Tinubu gobe Alhamis

    A gobe  Alhamis, 26 ga Oktoba, 2023 ne dai kotun kolin za ta yanke hukunci kan shari’ar jam’iyyar Labour da dan takararta na shugaban...

Recent Comments