Thursday, September 19, 2024
Home Muhimman Labarai An Karrama Dattijo Mai ƙirkire-ƙirƙire Da Bai Yi Boko Ba Da Digirin...

An Karrama Dattijo Mai ƙirkire-ƙirƙire Da Bai Yi Boko Ba Da Digirin Digirgir

Jami’ar jihar Gombe ta ƙarrma dattijon ɗan shekaru 70 Hadi Usman da digirin girmamawa na Dakta.

Jami’ar ta karrama dattijon ne a ranar Asabar yayin bikin yaye ɗaliban jami’ar.

Dattijon wanda bai taɓa karatu a makarantar boko ba yayi fice wajen ƙirkire-ƙirƙire na abubuwan fasaha da su ka haɗa da risho na girki mai amfani da ruwa maimakon man kanazir ko iskar gas.

Dattijon ya halarci bikin baje kolin fasaha na ƙasa da a ka gudanar shekarun baya saboda irin bajintar da ya nuna wajen ƙirkire-ƙirƙire.

Jami’ar jihar Gomben dai da ta karrama wannan dattijon dama ta dauke shi aiki.

Dattijo Hadi dai ya shiga sahun mashahuran mutane da jami’ar ta karrama da su ka haɗa da mataimakin shugaban kasa Kashim Shettima.

RELATED ARTICLES

Za A Fara Dandaƙe Masu Yi Wa Yara Fyaɗe

Ministan shari'a na Madagascar ya kare wani sabon kudiri a ranar Juma'a don hukunta masu yiwa kananan yara fyade. Kungiyar kare hakkin biladama ta ...

Kotu ta tabbatar da zaben Ahmadu Fintiri a matsayin gwamnan Adamawa

Kotun daukaka kara da ke zamanta a Abuja ta tabbatar da Ahmadu Fintiri na jam’iyyar PDP a matsayin gwamnan jihar Adamawa bayan ta yi...

Kotu koli ta tabbatar da zaben shugaban kasa Tinubu

A yau Alhamis ne kotun koli ta tabbatar da nasarar da shugaba Bola Tinubu ya samu a zaben shugaban kasa da aka gudanar a...
- Advertisment -

Most Popular

Za A Fara Dandaƙe Masu Yi Wa Yara Fyaɗe

Ministan shari'a na Madagascar ya kare wani sabon kudiri a ranar Juma'a don hukunta masu yiwa kananan yara fyade. Kungiyar kare hakkin biladama ta ...

Kotu ta tabbatar da zaben Ahmadu Fintiri a matsayin gwamnan Adamawa

Kotun daukaka kara da ke zamanta a Abuja ta tabbatar da Ahmadu Fintiri na jam’iyyar PDP a matsayin gwamnan jihar Adamawa bayan ta yi...

Kotu koli ta tabbatar da zaben shugaban kasa Tinubu

A yau Alhamis ne kotun koli ta tabbatar da nasarar da shugaba Bola Tinubu ya samu a zaben shugaban kasa da aka gudanar a...

Kotun koli za ta yanke hukunci kan zaben Tinubu gobe Alhamis

    A gobe  Alhamis, 26 ga Oktoba, 2023 ne dai kotun kolin za ta yanke hukunci kan shari’ar jam’iyyar Labour da dan takararta na shugaban...

Recent Comments