Thursday, September 19, 2024
Home Muhimman Labarai An yi garkuwa da dalibai mata biyar a jami'ar tarayya ta Dutsinma

An yi garkuwa da dalibai mata biyar a jami’ar tarayya ta Dutsinma

Wasu ‘yan bindiga sun kai farmaki a dakunan kwanan dalibai na jami’ar tarayya da ke Dutsinma (FUDMA), jihar Katsina, inda suka yi awon gaba da dalibai mata guda biyar.

Rahotanni sun bayyana cewa lamarin ya faru ne da sanyin safiyar yau  Laraba, a dakunan kwanan dalibai da ke a Dutsinma.

Har zuwa lokacin hada wannan rahoto, babu wani bayani dangane da halin da wadanda abin ya shafa ke ciki domin wadanda suka yi garkuwa da su ba su tuntubi iyalansu ba.

Shugaban sashin hulda da jama’a na jami’ar Habibu Umar Aminu ya tabbatar da cewa lamarin ya faru ne da misalin karfe biyu na safiyar ranar Laraba, inda ya kara da cewa ana ci gaba da kokarin kubutar da wadanda lamarin ya shafa.

Kakakin rundunar ‘yan sandan jihar Katsina, ASP Sadiq Aliyu Abubakar, ya ce an kama mutum daya da ake zargi da bayar da bayanai ga ‘yan ta’addan.

Ya bayyana cewa an kuma kama wasu mutane da ake zargin suna da hannu wajen yin garkuwa da daliban.

RELATED ARTICLES

Za A Fara Dandaƙe Masu Yi Wa Yara Fyaɗe

Ministan shari'a na Madagascar ya kare wani sabon kudiri a ranar Juma'a don hukunta masu yiwa kananan yara fyade. Kungiyar kare hakkin biladama ta ...

Kotu ta tabbatar da zaben Ahmadu Fintiri a matsayin gwamnan Adamawa

Kotun daukaka kara da ke zamanta a Abuja ta tabbatar da Ahmadu Fintiri na jam’iyyar PDP a matsayin gwamnan jihar Adamawa bayan ta yi...

Kotu koli ta tabbatar da zaben shugaban kasa Tinubu

A yau Alhamis ne kotun koli ta tabbatar da nasarar da shugaba Bola Tinubu ya samu a zaben shugaban kasa da aka gudanar a...
- Advertisment -

Most Popular

Za A Fara Dandaƙe Masu Yi Wa Yara Fyaɗe

Ministan shari'a na Madagascar ya kare wani sabon kudiri a ranar Juma'a don hukunta masu yiwa kananan yara fyade. Kungiyar kare hakkin biladama ta ...

Kotu ta tabbatar da zaben Ahmadu Fintiri a matsayin gwamnan Adamawa

Kotun daukaka kara da ke zamanta a Abuja ta tabbatar da Ahmadu Fintiri na jam’iyyar PDP a matsayin gwamnan jihar Adamawa bayan ta yi...

Kotu koli ta tabbatar da zaben shugaban kasa Tinubu

A yau Alhamis ne kotun koli ta tabbatar da nasarar da shugaba Bola Tinubu ya samu a zaben shugaban kasa da aka gudanar a...

Kotun koli za ta yanke hukunci kan zaben Tinubu gobe Alhamis

    A gobe  Alhamis, 26 ga Oktoba, 2023 ne dai kotun kolin za ta yanke hukunci kan shari’ar jam’iyyar Labour da dan takararta na shugaban...

Recent Comments