Thursday, September 19, 2024
Home Muhimman Labarai Atiku ya bukaci CBN da kada ya ƙara wa'adin daina karban tsofaffin...

Atiku ya bukaci CBN da kada ya ƙara wa’adin daina karban tsofaffin kuɗi.

Dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar, ya bukaci babban bankin Najeriya (CBN) da kada ya tsawaita wa’adin ranar 10 ga watan Fabreru na daina karban tsoffin takardun kudaden Naira.

An dai yi ta matsin lamba ga babban bankin kasa daga ‘yan Najeriya da dama da ya kara wa’adin yin musaya da takardun kudi na Naira saboda karancin kudin da aka sake wa fasali na N200, N500, da N1,000.

Tsohon mataimakin shugaban kasar, a wata sanarwa da ya fitar a ranar Alhamis, ya bukaci CBN da kada ya kara wa’adin ranar 10 ga watan Fabrairu.

Sai dai ya bukaci babban bankin kasa da ya gaggauta yin nazari a kan matakan da aka sanya na tabbatar da cewa an samu wadatuwar sabbin takardun kudi domin rage wahalhalun da ke addabar talakawa a fadin kasar nan, musamman mazauna karkara, wadanda ke bukatar kudi don gudanar da harkokinsu na kasuwancin.

Ya kuma yi zargin cewa ’yan siyasa da ke shirin yin magudi a babban zaben kasar nan na yin zagon-kasa don kara tsawaita wa’adin amfani da tsofaffin takardun kudi domin yin magudin zabe.

RELATED ARTICLES

Za A Fara Dandaƙe Masu Yi Wa Yara Fyaɗe

Ministan shari'a na Madagascar ya kare wani sabon kudiri a ranar Juma'a don hukunta masu yiwa kananan yara fyade. Kungiyar kare hakkin biladama ta ...

Kotu ta tabbatar da zaben Ahmadu Fintiri a matsayin gwamnan Adamawa

Kotun daukaka kara da ke zamanta a Abuja ta tabbatar da Ahmadu Fintiri na jam’iyyar PDP a matsayin gwamnan jihar Adamawa bayan ta yi...

Kotu koli ta tabbatar da zaben shugaban kasa Tinubu

A yau Alhamis ne kotun koli ta tabbatar da nasarar da shugaba Bola Tinubu ya samu a zaben shugaban kasa da aka gudanar a...
- Advertisment -

Most Popular

Za A Fara Dandaƙe Masu Yi Wa Yara Fyaɗe

Ministan shari'a na Madagascar ya kare wani sabon kudiri a ranar Juma'a don hukunta masu yiwa kananan yara fyade. Kungiyar kare hakkin biladama ta ...

Kotu ta tabbatar da zaben Ahmadu Fintiri a matsayin gwamnan Adamawa

Kotun daukaka kara da ke zamanta a Abuja ta tabbatar da Ahmadu Fintiri na jam’iyyar PDP a matsayin gwamnan jihar Adamawa bayan ta yi...

Kotu koli ta tabbatar da zaben shugaban kasa Tinubu

A yau Alhamis ne kotun koli ta tabbatar da nasarar da shugaba Bola Tinubu ya samu a zaben shugaban kasa da aka gudanar a...

Kotun koli za ta yanke hukunci kan zaben Tinubu gobe Alhamis

    A gobe  Alhamis, 26 ga Oktoba, 2023 ne dai kotun kolin za ta yanke hukunci kan shari’ar jam’iyyar Labour da dan takararta na shugaban...

Recent Comments