Thursday, September 19, 2024
Home Siyasa Dankwambo ya bukaci Inuwa ya daina kamfe muddin ya iya barazana

Dankwambo ya bukaci Inuwa ya daina kamfe muddin ya iya barazana

Tsohon gwamnan jihar Gombe Alhaji Ibrahim Hassan Dankwambo ya bukaci Gwamnan jihar ta Gombe Muhammad Inuwa Yahaya da ya daina kamfe muddin ya iya wa mutane barazana.

Dankwambo ya bayyana hakanne a yankin Suwa na karamar hukumar Balanga da ke kudncin jihar lokacin yakin neman zabe na dan takarar gwamnan jiha a Jam’iyar PDP, Muhammad Jibrin Barde.

Ibrahim Dankwambo ya yi zargin cewar jam’iyar APC na yi wa mutanen jihar barazana a yakin neman zabe da ta ke yi.

Ibrahim Dankwambo wanda ya bayyana cewar an tafka kuskure wajen zabin jam’iyar APC  a zabe da ya gabata, ya bukaci masu zabe a yankin da ka da su sake kuskuren zaben APC.

Dankwambo ya kara da cewar duk wanda bai ji a jikinsa ba a yanzu ya ji da kunnensa irin halin da a ka jefa jama’a a ciki.

A jawabinsa dan takarar gwamnan jihar a PDP Muhammad Jibrin Barde ya yi kira wa mutanen yankin da su tabbatar sun zabi yan takarar jam’iyar PDP a dukkan matakai a zabe da ke tafe.

Ya kuma yi al’kawarin daukan matakai da su ka dace wajen bunkasa harkar noma a yankin, ya na mai cewar zai tabbatar da bude madatsar ruwa ta Balanga a kwanaki 100 na farkon mulkinsa.

RELATED ARTICLES

Jami’yar APC ta Dakatar Da Ɗan takarar Gwamna Da Na Sanata A Taraba

Jam'iyyar APC a jihar Taraba ta kori ɗan takararta na gwamnan jihar a zaɓen 2023 da aka kammala David Sabo Kente kan zargin yi...

Gwamnoni shida sun gaza cin zabe don tsallakawa majalisar dattawa

Akalla gwamnoni shida masu barin gado sun gaza a yunkurinsu na tsallakawa majalisar dattawan Najeriya bayan wa’adinsu biyu na shekara takwas. Gwamnonin da ke barin...

Ofishin yaƙin neman zaɓen Tinubu ya ce a na yaɗa labaran ƙarya kan ɗan takaran

Ofishin yaƙin neman neman zaben ɗan takarar shugaban ƙasa a jam'iyar APC Bola Ahmed Tinubu ya ca ya lura da wasu shafukan labarai na...
- Advertisment -

Most Popular

Za A Fara Dandaƙe Masu Yi Wa Yara Fyaɗe

Ministan shari'a na Madagascar ya kare wani sabon kudiri a ranar Juma'a don hukunta masu yiwa kananan yara fyade. Kungiyar kare hakkin biladama ta ...

Kotu ta tabbatar da zaben Ahmadu Fintiri a matsayin gwamnan Adamawa

Kotun daukaka kara da ke zamanta a Abuja ta tabbatar da Ahmadu Fintiri na jam’iyyar PDP a matsayin gwamnan jihar Adamawa bayan ta yi...

Kotu koli ta tabbatar da zaben shugaban kasa Tinubu

A yau Alhamis ne kotun koli ta tabbatar da nasarar da shugaba Bola Tinubu ya samu a zaben shugaban kasa da aka gudanar a...

Kotun koli za ta yanke hukunci kan zaben Tinubu gobe Alhamis

    A gobe  Alhamis, 26 ga Oktoba, 2023 ne dai kotun kolin za ta yanke hukunci kan shari’ar jam’iyyar Labour da dan takararta na shugaban...

Recent Comments