Friday, September 13, 2024
Home Muhimman Labarai Gwamnoni shida sun gaza cin zabe don tsallakawa majalisar dattawa

Gwamnoni shida sun gaza cin zabe don tsallakawa majalisar dattawa

Akalla gwamnoni shida masu barin gado sun gaza a yunkurinsu na tsallakawa majalisar dattawan Najeriya bayan wa’adinsu biyu na shekara takwas.
Gwamnonin da ke barin gado sun sha kaye a zaben ‘yan majalisar dokokin kasa da aka gudanar ranar 25 ga watan Fabrairu a mazabunsu na majalisar dattawa.
Tun bayan da Najeriya ta koma kan turbar dimokuradiyya a shekarar 1999 bayan mulkin soja na tsawon shekaru, majalisar dokokin dattawa na zama a matsayin ‘gidan ritaya’ na tsaffin gwamnoni.
Gwamnonin da suka yi rashin nasara kawo yanzu sun hada da Ben Ayade (Cross River), Samuel Ortom na jihar Benue, Ifeanyi Ugwuanyi na Enugu, Darius Ishaku na Taraba, Simon Lalong (Plateau), Okezie Ikpeazu (Abia) da Atiku Bagudu na Kebbi.
Gwamna Dave Umahi na Jihar Ebonyi da Gwamna Abubakar Bello, na Jihar Neja duk sun samu kujerunsu a Majalisar Dattawa.
A yanzu a na dakon sakamakon gwamnan jihar Sokoto Aminu Tambuwa wanda shima ya tsaya zaben sanata bayan da ya ke shirin kare wa’adin sa na biyu a mulki.

RELATED ARTICLES

Za A Fara Dandaƙe Masu Yi Wa Yara Fyaɗe

Ministan shari'a na Madagascar ya kare wani sabon kudiri a ranar Juma'a don hukunta masu yiwa kananan yara fyade. Kungiyar kare hakkin biladama ta ...

Kotu ta tabbatar da zaben Ahmadu Fintiri a matsayin gwamnan Adamawa

Kotun daukaka kara da ke zamanta a Abuja ta tabbatar da Ahmadu Fintiri na jam’iyyar PDP a matsayin gwamnan jihar Adamawa bayan ta yi...

Kotu koli ta tabbatar da zaben shugaban kasa Tinubu

A yau Alhamis ne kotun koli ta tabbatar da nasarar da shugaba Bola Tinubu ya samu a zaben shugaban kasa da aka gudanar a...
- Advertisment -

Most Popular

Za A Fara Dandaƙe Masu Yi Wa Yara Fyaɗe

Ministan shari'a na Madagascar ya kare wani sabon kudiri a ranar Juma'a don hukunta masu yiwa kananan yara fyade. Kungiyar kare hakkin biladama ta ...

Kotu ta tabbatar da zaben Ahmadu Fintiri a matsayin gwamnan Adamawa

Kotun daukaka kara da ke zamanta a Abuja ta tabbatar da Ahmadu Fintiri na jam’iyyar PDP a matsayin gwamnan jihar Adamawa bayan ta yi...

Kotu koli ta tabbatar da zaben shugaban kasa Tinubu

A yau Alhamis ne kotun koli ta tabbatar da nasarar da shugaba Bola Tinubu ya samu a zaben shugaban kasa da aka gudanar a...

Kotun koli za ta yanke hukunci kan zaben Tinubu gobe Alhamis

    A gobe  Alhamis, 26 ga Oktoba, 2023 ne dai kotun kolin za ta yanke hukunci kan shari’ar jam’iyyar Labour da dan takararta na shugaban...

Recent Comments