Thursday, September 19, 2024
Home Tsaro Hukumar tsaro ta DSS ta damke masu sayar da sabbin kudi

Hukumar tsaro ta DSS ta damke masu sayar da sabbin kudi

Hukumar tsaro ta farin kaya ta DSS, ta sanar da kama wasu da a ka zarga aikata laifukan sayar da sababbin takardun kudin da gwamnati ta fitar a sassan Najeriya.

Wannan na cikin wata sanarwa da hukumar tsaron ta fitar ta hannun kakakinta Peter Afunanya a ranar Litinin a Abuja babban birnin kasar.

Ya ce jami’an hukumar ne suka damke gungun masu aikata laifin yayin da suke tsakiyar hada-hada.

Ya kuma ce, binciken su ya nuna cewa wasu jami’an bankunan kasuwanci na taimaka wa masu aikata wannan zagon kasar da ake wa tattalin arziki.

Hukumar ta gargadi al’umma da su taimaka wa jami’anta da bayanan dukkan wuraren da suka san ana yin wannan haramtaccen cinikin.

RELATED ARTICLES
- Advertisment -

Most Popular

Za A Fara Dandaƙe Masu Yi Wa Yara Fyaɗe

Ministan shari'a na Madagascar ya kare wani sabon kudiri a ranar Juma'a don hukunta masu yiwa kananan yara fyade. Kungiyar kare hakkin biladama ta ...

Kotu ta tabbatar da zaben Ahmadu Fintiri a matsayin gwamnan Adamawa

Kotun daukaka kara da ke zamanta a Abuja ta tabbatar da Ahmadu Fintiri na jam’iyyar PDP a matsayin gwamnan jihar Adamawa bayan ta yi...

Kotu koli ta tabbatar da zaben shugaban kasa Tinubu

A yau Alhamis ne kotun koli ta tabbatar da nasarar da shugaba Bola Tinubu ya samu a zaben shugaban kasa da aka gudanar a...

Kotun koli za ta yanke hukunci kan zaben Tinubu gobe Alhamis

    A gobe  Alhamis, 26 ga Oktoba, 2023 ne dai kotun kolin za ta yanke hukunci kan shari’ar jam’iyyar Labour da dan takararta na shugaban...

Recent Comments