Thursday, September 19, 2024
Home Shari'a Kotu Ta Kori karar Neman Hana Inuwa Takarar Gwaman Gombe

Kotu Ta Kori karar Neman Hana Inuwa Takarar Gwaman Gombe

Kotu Ta Kori karar Da Ke Neman Hana Inuwa Takarar Gwaman Gombe

A jiya ne wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta yi watsi da karar da a ka shigar gabanta inda a ke bukatar ta hana gwamna Mohammed Inuwa Yahaya takara jam’iyyar APC a zaben gwamnan jihar Gombe da ke tafe.

Mai shari’a Binta Nyako, yayin da take yanke hukunci, ta yi watsi da zargin da ake yi wa gwamnan na mika bayanan karya ga hukumar zabe mai zaman kanta.

Jam’iyyar adawa PDP da wasu jiga-jiganta biyu a jihar, Muhammed Jibrin Barde da Timothy Danlele ne suka gabatar da karar a gaban kotun.

Musamman, Barde da Danlele, ta bakin lauyansu, Johnson Usman, sun yi zargin cewa gwamnan ya yi karya a cikin takardun da ya gabatar a gaban INEC.

Sun ce gwamnan bai gabatar da bayanan Gaskiya ba don haka ya kamata a kore shi daga shiga zaben gwamnan da za a yi a ranar 11 ga watan Maris.

Sai dai kotun ta yi watsi da karar bisa rashin cancanta.

RELATED ARTICLES

Za A Fara Dandaƙe Masu Yi Wa Yara Fyaɗe

Ministan shari'a na Madagascar ya kare wani sabon kudiri a ranar Juma'a don hukunta masu yiwa kananan yara fyade. Kungiyar kare hakkin biladama ta ...

An yankewa likita hukuncin ɗaurin rai-da-rai a kan fyade

Kotun da ke shari’ar laifukan lalata da cin zarafi a jihar Legas da ke zaune a Ikeja ta yanke hukuncin daurin rai-da-rai  daraktan kula...

Jami’yar APC ta Dakatar Da Ɗan takarar Gwamna Da Na Sanata A Taraba

Jam'iyyar APC a jihar Taraba ta kori ɗan takararta na gwamnan jihar a zaɓen 2023 da aka kammala David Sabo Kente kan zargin yi...
- Advertisment -

Most Popular

Za A Fara Dandaƙe Masu Yi Wa Yara Fyaɗe

Ministan shari'a na Madagascar ya kare wani sabon kudiri a ranar Juma'a don hukunta masu yiwa kananan yara fyade. Kungiyar kare hakkin biladama ta ...

Kotu ta tabbatar da zaben Ahmadu Fintiri a matsayin gwamnan Adamawa

Kotun daukaka kara da ke zamanta a Abuja ta tabbatar da Ahmadu Fintiri na jam’iyyar PDP a matsayin gwamnan jihar Adamawa bayan ta yi...

Kotu koli ta tabbatar da zaben shugaban kasa Tinubu

A yau Alhamis ne kotun koli ta tabbatar da nasarar da shugaba Bola Tinubu ya samu a zaben shugaban kasa da aka gudanar a...

Kotun koli za ta yanke hukunci kan zaben Tinubu gobe Alhamis

    A gobe  Alhamis, 26 ga Oktoba, 2023 ne dai kotun kolin za ta yanke hukunci kan shari’ar jam’iyyar Labour da dan takararta na shugaban...

Recent Comments