Friday, September 13, 2024
Home Kasuwanci NNPC ya nemi afuwan 'yan Najeriya kan karancin man fetur

NNPC ya nemi afuwan ‘yan Najeriya kan karancin man fetur

Shugaban Kamfanin mai na kasa, NNPC ya bai wa ‘yan Najeriya hakuri kan matsin da suka sake tsintar kansu sakamakon karancin man fetur.

Shugaban kamfanin man, Mele Kolo Kyari ya tabbatar wa manema labarai cewa ana sa ran matsalar ta yanke cikin ƴan kwanaki kaɗan masu zuwa.

Kalaman Mele Kyari na zuwa ne a daidai lokacin da al’umma ke ci gaba da fuskantar dogayen layukan mai, musamman a manyan biranen ƙasar.

Matsalar ta man fetur, wadda ta ƙi ci ta ƙi cinyewa tun a shekarar da ta gabata, na ci gaba da jefa al’ummacikin garari, yayin da babban zaɓen ƙasa ke ƙaratowa.

Sai dai Mele Kyari ya ce cikin kwanaki biyu masu zuwa za a samu sauki ko da wahalar bata kare ba baki ɗaya domin hukumomi sun ɗauki matakan da suka dace domin ganin an shawo kan matsalar.

RELATED ARTICLES

Ba za mu kara wa’adin daina karban tsoffin kudi ba- CBN

Babban Bankin Najeriya (CBN) ya ce ba za a kara wa’adin ranar 31 ga watan Junairun wannan shekara ba domin daina karban...

Mataikin shugaban kasa Ya Mutu a Indiya

Mataimakin Shugaban Kasar Gambiya, Badara Joof, ya rasu a kasar Indiya. Shugaban Kasar, Adama Barrow ne ya sanar da...

Wani Mutum Ya kai ƙarar Hadiza Gabon Saboda Ta ƙi Auransa

Wani ma’aikacin gwamnati Bala Musa mai shekaru 48 a duniya a ranar Litinin ya maka wata jarumar fina-finan Kannywood Hadiza Gabon a...
- Advertisment -

Most Popular

Za A Fara Dandaƙe Masu Yi Wa Yara Fyaɗe

Ministan shari'a na Madagascar ya kare wani sabon kudiri a ranar Juma'a don hukunta masu yiwa kananan yara fyade. Kungiyar kare hakkin biladama ta ...

Kotu ta tabbatar da zaben Ahmadu Fintiri a matsayin gwamnan Adamawa

Kotun daukaka kara da ke zamanta a Abuja ta tabbatar da Ahmadu Fintiri na jam’iyyar PDP a matsayin gwamnan jihar Adamawa bayan ta yi...

Kotu koli ta tabbatar da zaben shugaban kasa Tinubu

A yau Alhamis ne kotun koli ta tabbatar da nasarar da shugaba Bola Tinubu ya samu a zaben shugaban kasa da aka gudanar a...

Kotun koli za ta yanke hukunci kan zaben Tinubu gobe Alhamis

    A gobe  Alhamis, 26 ga Oktoba, 2023 ne dai kotun kolin za ta yanke hukunci kan shari’ar jam’iyyar Labour da dan takararta na shugaban...

Recent Comments