Thursday, September 19, 2024
Home Muhimman Labarai Yan sanda sun ceto mutum biyu da a ka yi garkuwa da...

Yan sanda sun ceto mutum biyu da a ka yi garkuwa da su a Gombe

Rundunar ‘yan sandan jihar Gombe ta ce ta ceto wasu mutane biyu da aka yi garkuwa da su a yankin Shabewa da ke karamar hukumar Dukku a jihar Gombe.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da ASP Mahid Muazu Abubakar ya fitar Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar Gombe.

Sanarwar ta ce rundunar ta samu sahihan bayanan sirri tare da kaddamar da aikin ceto, tare da goyon bayan mambobin kungiyoyin mafarauta da ’yan banga da ke kusa inda aka gano wuraren da ake zargin masu garkuwa da mutanen na fake.

Aikin ceton ya dauki tsawon sa’o’i 48, inda ya a ka yi nasarar ceto mutanen biyu da aka yi garkuwar da su ba tare da biyan kudin fansa ba a safiyar ranar Litinin.

A ranar 8 ga watan Oktoba wasu da ake zargin masu garkuwa da mutane ne suka kai farmaki gidan Umar Sambo na yankin Shabewa a Dukku, karamar hukumar Dukku, dauke da bindigogi da wasu muggan makamai.

Sun yi garkuwa da daya daga cikin matansa mai suna Amina Usman Aliyu da dan uwansa Mustapha Sambo.

A halin da ake ciki, kwamishinan ‘yan sandan jihar ya bukaci mazauna yankin da su kwantar da hankulansu tare da baiwa hukumomin ‘yan sanda hadin kai ta hanyar samar da bayanai masu amfani don dakile ayyukan miyagun ayyuka a jihar.

RELATED ARTICLES

Za A Fara Dandaƙe Masu Yi Wa Yara Fyaɗe

Ministan shari'a na Madagascar ya kare wani sabon kudiri a ranar Juma'a don hukunta masu yiwa kananan yara fyade. Kungiyar kare hakkin biladama ta ...

Kotu ta tabbatar da zaben Ahmadu Fintiri a matsayin gwamnan Adamawa

Kotun daukaka kara da ke zamanta a Abuja ta tabbatar da Ahmadu Fintiri na jam’iyyar PDP a matsayin gwamnan jihar Adamawa bayan ta yi...

Kotu koli ta tabbatar da zaben shugaban kasa Tinubu

A yau Alhamis ne kotun koli ta tabbatar da nasarar da shugaba Bola Tinubu ya samu a zaben shugaban kasa da aka gudanar a...
- Advertisment -

Most Popular

Za A Fara Dandaƙe Masu Yi Wa Yara Fyaɗe

Ministan shari'a na Madagascar ya kare wani sabon kudiri a ranar Juma'a don hukunta masu yiwa kananan yara fyade. Kungiyar kare hakkin biladama ta ...

Kotu ta tabbatar da zaben Ahmadu Fintiri a matsayin gwamnan Adamawa

Kotun daukaka kara da ke zamanta a Abuja ta tabbatar da Ahmadu Fintiri na jam’iyyar PDP a matsayin gwamnan jihar Adamawa bayan ta yi...

Kotu koli ta tabbatar da zaben shugaban kasa Tinubu

A yau Alhamis ne kotun koli ta tabbatar da nasarar da shugaba Bola Tinubu ya samu a zaben shugaban kasa da aka gudanar a...

Kotun koli za ta yanke hukunci kan zaben Tinubu gobe Alhamis

    A gobe  Alhamis, 26 ga Oktoba, 2023 ne dai kotun kolin za ta yanke hukunci kan shari’ar jam’iyyar Labour da dan takararta na shugaban...

Recent Comments